Sabuwar Rayuwa Bayan Yaki
Saurara a: Apple Podcast | Spotify | RSS
Christie Garba mace ce mai shekaru 38, uwa ga yara bakwai, wadda ke zaune a Billiri, Jihar Gombe, a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya. Ta kasance tana zaune a Jihar Yobe tare da iyalinta kafin rikicin Boko Haram ya addabi yankin. A wancan lokacin, hare-hare sun riga sun faru a wasu wurare kusa da su, amma ba su kai ga al’ummarsu kai tsaye ba.
Christie da iyalinta sun zauna kimanin watanni huɗu bayan hare-haren sun fara, amma yayin da rikicin ya ƙaru, sojoji suka gargadi mazauna yankin cewa lamarin ya yi tsanani sosai, ba zai yiwu su ci gaba da zama ba. Dokokin hana fita (curfew) da suka biyo baya sun sa rayuwar yau da kullum ta zama mai matuƙar wahala.
A wannan shirin na #BirbishinRikici mun ba da labarin yadda Christie da iyalinta suka koma Jihar Gombe da kuma yadda ta yi rayuwa ta hanyar fara sabon kasuwanci.
Mai Gabatarwa: Rukayya Saeed
Marubuciya: Sabiqah Bello
Muryoyin Shiri: Sabiqah Bello
Fassara: Rukayya Saeed
Edita: Aliyu Dahiru
Furodusa: Mu’azu Muhammad
Babban Furodusa: Anthony Asemota
Babban Mashiryi: Ahmad Salkida
Christie Garba, a 38-year-old mother of seven from Billiri, Gombe, in Northeastern Nigeria, was originally residing in Yobe with her family when the Boko Haram crisis began affecting their region. Initially, their community wasn't directly impacted, but as the conflict worsened, military advisories and curfews made daily life untenable, prompting her relocation.
The discussed episode of #BirbishinRikici narrates Christie's transition to Gombe and her pursuit of a new livelihood through starting a business amid the tumultuous backdrop. This narrative was presented by Rukayya Saeed, written and voiced by Sabiqah Bello, with editorial input by Aliyu Dahiru, and production oversight by Mu’azu Muhammad and Anthony Asemota.
Support Our Journalism
There are millions of ordinary people affected by conflict in Africa whose stories are missing in the mainstream media. HumAngle is determined to tell those challenging and under-reported stories, hoping that the people impacted by these conflicts will find the safety and security they deserve.
To ensure that we continue to provide public service coverage, we have a small favour to ask you. We want you to be part of our journalistic endeavour by contributing a token to us.
Your donation will further promote a robust, free, and independent media.
Donate HereStay Closer To The Stories That Matter



